Home General An gudanar da Jana’idar Dan Zago

An gudanar da Jana’idar Dan Zago

An gudanar da jana’izar Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Dan Zago, tsohon shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano.

An gudanar da jana’izar a Kofar Kudu, dake fadar mai martaba Sarkin Kano Dr. Muhammadu Sanusi II.

Jana’izar ta samu halartar fitattun mutane da suka hadar da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II, da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Dan Zago, ya rasu yana da shekaru 74, sannan ya bar Mata 4 da yaya 37 sai kuma jikoki da dama.

Bayan kammala jana’izar Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya jagoranci zuwa gidan marigayin, domin yi musu ta’aziyyar rashin da suka yi.

Sauran wadanda suka je ta’aziyyar sun hadar da tsohon gwamnan Kano Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso da mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo da shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Ismail Jibrin Falgore sun shiga gidan marigayin inda suka yi addu’oi domin nema masa gafarar Allah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp