Home General Gwamnan Kano ya haramta sanya dalibai aikin wahala a makarantu

Gwamnan Kano ya haramta sanya dalibai aikin wahala a makarantu

Gwamnan jihar Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya gargadi malamai da su daina tilastawa dalibai yin aikace-aikace masu wahala a ciki ko a wajen makaranta

Haramcin na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sunusi Bature Dawakin-Tofa, ya fitar aka raba manema labarai a jihar kano.

Gwamnan ya jaddada cewa makarantu wuraren karatu ne na koyar da ilimi da tarbiyya, ba wuraren yin aikin wahala ba.

Yayin wata ziyarar bazata da ya ka makarantar koyon harshen larabci (School for Arabic Studies) Kano, gwamnan ya tarar da wasu dalibai suna tonon ramin bututun bayan gida.

Inda cikin fushi, gwamnan ya tambayi shugaban makarantar dalilin da ya sa aka ba dalibai irin wannan aiki.

Shugaban makarantar ya shaidawa gwamna cewa aikin an ba su ne bayan an tashi daga makaranta.

Sai dai nan take gwamnan ya bayar da umarnin dakatar da yaran da aka sa aikin, ya kuma tabbatar wa shugabannin makarantar cewa gwamnatinsa za ta gyara dukkan gine-ginen da suka lalace, har da masallacin da ke cikin makarantar.

Haka kuma, ya bada umarni cewa duk wata bukata ta gyaran makaranta a mikata ga Ma’aikatar Ilimi ko ofishinsa domin aiwatarwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp