Hukumar Kwallon Kwando ta Najeriya (NBBF) a ranar Litinin ta fitar da jerin sunayen ‘yan wasa 12 na karshe na D’Tigers a gasar FIBA AfroBasket na uku da za a yi a Tripoli, Libya, daga 21-23 ga Fabrairu 2025.
A farkon watan nan ne dai NBBF ta sanar da jerin sunayen mutane 24 na D’Tigers, wanda a yanzu an rage shi da kashi 50%.
Tawagar da aka zaba sun hada da gwanayen ’yan wasa da kwararru masu tasowa, duk a shirye-shirye su wakilci Najeriya a fagen wasan duniya.
Babban koci, Abdulrahman Mohammed, wanda ya jagoranci D’Tigers a zango na farko, zai ci gaba da rike mukaminsa, yayin da tsohon dan wasan Najeriya Deji Akindele da Isikaku Ikenna Smart, mataimakin kocin kungiyar Portland Trail Blazers na kungiyar Kwando ta (NBA) ne za su taimaka masa.
Read Also:
Masu horar da ‘yan wasan da ma’aikatansu, tare da ‘yan wasan, sun tashi daga wurarensu a ranar Litinin, ida ake sa ran isa birnin Tripoli ranar 18 ga watan Fabrairu.
A yammacin ranar Talata ne ake sa ran kungiyar za ta gudanar da atisayenta na farko, yayin da suke ci gaba da kammala shirye-shiryensu na tunkarar muhimman wasannin da ke gaba.
Ƴan wasan D’Tigers 12 da aka gayyata:
Zaid Hearst (Zamora, Spain)
Mike Nuga (Valmiera Glass, Latvia)
Ike Nwamu (CCMB, France) – Team Captain
Caleb Agada (Avtador, Russia)
Ugochukwu Simon (Virtus Ragusa, Italy)
Ifeanyi Koko (Rivers Hoopers)
Ibe Agu (Customs, Nigeria)
Abdul Malik Abu (Arriva P. Cukier, Poland)
Christian Mekowulu (Akita Northern Happinets, Japan)
Talib Zanna (KK Cibona, Croatia)
Kaodirichi Akobundu-Ehiogu (Pallacanestro Varese, Italy)
Jason Jitoboh (Vellaznimi, Kosovo)
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 2 hours 24 minutes 14 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 4 hours 5 minutes 39 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com