Shugaban ‘yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda a gabashin Congo ya yi watsi da tayin da Kinshasa da Kigali suka yi na tsagaita wuta cikin gaggawa, yayin da dakarunsa suka shiga cikin yankunan gabashin Congo tare da sake ƙwace garin Walikale mai muhimmanci.
Bayan karɓe ikon wasu manyan birane guda biyu a gabashin ƙasar ta Congo, birnin na Walikale dake da tazarar kilomita 125 daga babban birnin ƙasar Kinshasa wanda ke ɗaya daga cikin masu tarin arzikin ma’adanai da ya shiga kwamar ƴan tawayen na M23.
Read Also:
Garin mai yawan al’umma 15,000 ya faɗa ƙarƙashin ikon ƴan tawayen ne bayan wani ƙazamin faɗa da ya ɓarke a tsakaninsu da dakarun sojin ƙasar ta Jamhuriyyar Congo.
Faɗan, wanda ya samo asali daga kisan kiyashi da aka yi a kasar Rwanda a shekarar 1994 da kuma gogayya kan mallakar arzikin albarkatun ƙasa, shi ne mafi muni a gabashin Congo tun bayan yakin shekarar 1998 zuwa 2003 wanda ya yi sanadin mutuwar miliyoyin mutane.
A yayin da masana suka bayyana cewa wannan yaƙin da ƙasashen Congo da Rwanda da kuma Burundi suka tsunduma cikinsa a wannan shekara, ya munana bisa yadda yake ƙoƙarin bazuwa yankin baki ɗayansa.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 20 hours 23 minutes 29 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 4 minutes 54 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com