Home General M23 ta sake ƙwace wani yanki a Congo bayan watsi da kiran...

M23 ta sake ƙwace wani yanki a Congo bayan watsi da kiran tsagaita wuta

Shugaban ‘yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda a gabashin Congo ya yi watsi da tayin da Kinshasa da Kigali suka yi na tsagaita wuta cikin gaggawa, yayin da dakarunsa suka shiga cikin yankunan gabashin Congo tare da sake ƙwace garin Walikale mai muhimmanci.

Bayan karɓe ikon wasu manyan birane guda biyu a gabashin ƙasar ta Congo, birnin na Walikale dake da tazarar kilomita 125 daga babban birnin ƙasar Kinshasa wanda ke ɗaya daga cikin masu tarin arzikin ma’adanai da ya shiga kwamar ƴan tawayen na M23.

Garin mai yawan al’umma 15,000 ya faɗa ƙarƙashin ikon ƴan tawayen ne bayan wani ƙazamin faɗa da ya ɓarke a tsakaninsu da dakarun sojin ƙasar ta Jamhuriyyar Congo.

Faɗan, wanda ya samo asali daga kisan kiyashi da aka yi a kasar Rwanda a shekarar 1994 da kuma gogayya kan mallakar arzikin albarkatun ƙasa, shi ne mafi muni a gabashin Congo tun bayan yakin shekarar 1998 zuwa 2003 wanda ya yi sanadin mutuwar miliyoyin mutane.

A yayin da masana suka bayyana cewa wannan yaƙin da ƙasashen Congo da Rwanda da kuma Burundi suka tsunduma cikinsa a wannan shekara, ya munana bisa yadda yake ƙoƙarin bazuwa yankin baki ɗayansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp