Akalla mutane 30 ne aka kashe a fadan da aka yi a wani gari da ke arewacin Sudan ta Kudu wanda wasu gungun matasa ɗauke da makamai suka mamaye na wani dan lokaci bayan wani farmakin da suka kai na shanu, kamar yadda wani jami’in yankin ya sanar a jiya Alhamis.
Lamarin ya faru a yankin arewacin Ruweng a farkon mako lokacin da wasu matasa dauke da makamai suka sace raguna kafin jami’an tsaro su fatattake su, in ji Simon Chol Mialith, ministan yada labaran yankin.
Washegari, kamar yadda ya shaida wa AFP, kungiyar matasan ta dawo da yawa inda suka kai hari a garin Abiemnom.
Read Also:
Ministan ya kara da cewa, “matasa da jami’an tsaro sun yi kokarin kare birnin amma matasa dauke da makamai suka mamaye su.
A ranar Larabar da ta gabata ce Dakarun tsaron Sudan ta Kudu (SSPDF) suka fatattaki ‘yan kungiyar da ke dauke da makamai tare da samun kwanciyar hankali, in ji Mialith. “Akwai matattu talatin da kuma jikkata kusan arba’in,” in ji shi, ba tare da yin karin bayani ba.
Kafofin yada labaran cikin gida sun ruwaito cewa wasu daga cikin wadanda aka kashe na kungiyar ne, amma kamfanin dillancin labaran AFP ya kasa tabbatar da wannan labarin.
Rikici tsakanin makiyaya da al’ummomin da ba sa zaman kashe wando dai ya zama ruwan dare a Sudan ta Kudu, sai dai wadannan al’amura na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin siyasa ya tsananta.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 14 hours 33 minutes 32 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 14 minutes 57 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com