Home General Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta...

Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta Kudu

Akalla mutane 30 ne aka kashe a fadan da aka yi a wani gari da ke arewacin Sudan ta Kudu wanda wasu gungun matasa ɗauke da makamai suka mamaye na wani dan lokaci bayan wani farmakin da suka kai na shanu, kamar yadda wani jami’in yankin ya sanar a jiya Alhamis.

Lamarin ya faru a yankin arewacin Ruweng a farkon mako lokacin da wasu matasa dauke da makamai suka sace raguna kafin jami’an tsaro su fatattake su, in ji Simon Chol Mialith, ministan yada labaran yankin.

Washegari, kamar yadda ya shaida wa AFP, kungiyar matasan ta dawo da yawa inda suka kai hari a garin Abiemnom.

Ministan ya kara da cewa, “matasa da jami’an tsaro sun yi kokarin kare birnin amma matasa dauke da makamai suka mamaye su.

A ranar Larabar da ta gabata ce Dakarun tsaron Sudan ta Kudu (SSPDF) suka fatattaki ‘yan kungiyar da ke dauke da makamai tare da samun kwanciyar hankali, in ji Mialith. “Akwai matattu talatin da kuma jikkata kusan arba’in,” ​​in ji shi, ba tare da yin karin bayani ba.

Kafofin yada labaran cikin gida sun ruwaito cewa wasu daga cikin wadanda aka kashe na kungiyar ne, amma kamfanin dillancin labaran AFP ya kasa tabbatar da wannan labarin.

Rikici tsakanin makiyaya da al’ummomin da ba sa zaman kashe wando dai ya zama ruwan dare a Sudan ta Kudu, sai dai wadannan al’amura na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin siyasa ya tsananta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp