Motar da ke ɗauke da ƴanwasan Kano da masu horar da su a gasar wasanni ta ƙasa wato National Sport Festival ta Najeriya ta yi hatsarin a hanyar komawa gida, inda rahotanni suka ce mutum 22 daga cikinsu sun rasu, sannan wasu sun jikkata.
Lamarin ya faru kimanin kilomita 50 zuwa Kano a yau Asabar bayan da motar ta taso daga jihar Ogun da ke kudu maso yammacin ƙasar bayan an kammala wasannin a ranar Juma’a.
Shi ma Kwamishinan matasa da wasanni na jihar, Mustapha Rabiu Kwankwaso ya bayyana kaɗuwarsa kan hatsarin, inda ya ce lamari ne da ya taɓa jihar baki ɗaya.
A wata sanarwa da kwamishinan ya fitar, ya ce “wannan lamarin abin tayar da hakali ne matuƙa. Muna jajanta wa ƴanuwa da iyalan waɗanda suka rasu da ma mutanen jihar Kano baki ɗaya,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ɗauki ɗawainiyar kula da sauran waɗanda suka ji raunuka.
WADANNAN SUNE SUKA RASU:
1. Abdurrahman Muhd
2. Abdul’aziz Auwalu
3. Nasiru Adam
4. Ibrahim Salisu
5. Bashir Bello (Yar gaya)
6. Imamumalik Umar
7. Bilal Salisu (Jegus Photography)
8. Ashiru Shu’aibu
9. Abdussamad Rabiu
10. Abubakar Isma’il Yakubu
11. Bello Muhd
12. Usaini Garba
13. Isah Usman Aliyu
14. Isah Ibrahim
15. Abdullahi Saleh Trigger
16. Nasiru Abdullahi
17. Aminu Muhammad
18. Shehu Saidu
19. Usman Muhammad
20. Sani Yusuf
21. Muhammad Aminu (Alaja)
22. Hamal Dahiru
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1461 days 22 hours 33 minutes 6 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 14 minutes 31 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com