Home General Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 ‘yan asalin Kano

Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 ‘yan asalin Kano

Motar da ke ɗauke da ƴanwasan Kano da masu horar da su a gasar wasanni ta ƙasa wato National Sport Festival ta Najeriya ta yi hatsarin a hanyar komawa gida, inda rahotanni suka ce mutum 22 daga cikinsu sun rasu, sannan wasu sun jikkata.

Lamarin ya faru kimanin kilomita 50 zuwa Kano a yau Asabar bayan  da motar ta taso daga jihar Ogun da ke kudu maso yammacin ƙasar bayan an kammala wasannin a ranar Juma’a.

Shi ma Kwamishinan matasa da wasanni na jihar, Mustapha Rabiu Kwankwaso ya bayyana kaɗuwarsa kan hatsarin, inda ya ce lamari ne da ya taɓa jihar baki ɗaya.

A wata sanarwa da kwamishinan ya fitar, ya ce “wannan lamarin abin tayar da hakali ne matuƙa. Muna jajanta wa ƴanuwa da iyalan waɗanda suka rasu da ma mutanen jihar Kano baki ɗaya,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ɗauki ɗawainiyar kula da sauran waɗanda suka ji raunuka.

WADANNAN SUNE SUKA RASU:
1. Abdurrahman Muhd
2. Abdul’aziz Auwalu
3. Nasiru Adam
4. ⁠Ibrahim Salisu
5. ⁠Bashir Bello (Yar gaya)
6. ⁠Imamumalik Umar
7. ⁠Bilal Salisu (Jegus Photography)
8. ⁠Ashiru Shu’aibu
9. ⁠Abdussamad Rabiu
10. ⁠Abubakar Isma’il Yakubu
11. ⁠Bello Muhd
12. ⁠Usaini Garba
13. ⁠Isah Usman Aliyu
14. ⁠Isah Ibrahim
15. ⁠Abdullahi Saleh Trigger
16. ⁠Nasiru Abdullahi
17. ⁠Aminu Muhammad
18. ⁠Shehu Saidu
19. ⁠Usman Muhammad
20. Sani Yusuf
21. ⁠Muhammad Aminu (Alaja)
22. Hamal Dahiru

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp