Home General Gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe

Gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe

Wata mummunar gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe inda ta ƙone wani ɓangare na kasuwar da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Gobarar ta lalata rumfuna a kasuwar wadda ke hada-hada mako-mako, lamarin da ya jefa, ɗimbin mutanen da suka dogara da kasuwar wajen harkokin rayuwarsu cikin mawuyacin hali.

Gobarar dai ta tashi ne jiya da yamma daf da lokacin buɗa bakin azumin ramadan, inda ta mamaye rumfuna 135 wadanda aƙasarinsu na kwano da katako ne wasu kuma na itace da kara.

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe, Dr. Muhammad Goje ya tabbatar da aukuwar wannan gobara.

Ya ƙara da cewa gobarar ba ta shiga shaguna ba kuma ba a rasa rai ko ɗaya ,a a gobarar.

Dr Muhammad Goje ya ƙara da cewa wannan tashin gobara a kasuwar Fika itace ta uku da aka samu a kasuwanni daban-daban cikin kasa da wata daya a jihar ciki harda kasuwar Bukarti, inda rumfuna kusan dari suka ƙone, sai kuma kasuwar Fuchimiran a ƙaramar hukumar Geidam, inda rufunan da gidajen mutane da dama suka kone.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓe
X whatsapp