Home DUNIYA Gwamnatin Habasha na fatan warware rikicin arewacin kasar.

Gwamnatin Habasha na fatan warware rikicin arewacin kasar.

Jakadan Amurka a yankin Afirka Mike Hammer, ya gana da mataimakin firaministan kasar Habasha Demeke Mekonnen a birnin Addis Ababa a ranar Juma’a, a kokarinsa na kawo karshen rikici a arewacin kasar.

Bayan wata ziyara da ya kai a watan Satumba na shekarar nan, Mike Hammer ya koma yankin tun ranar 3 ga watan Oktoba, da fatan ganin an dakatar da tashin hankali a arewacin Habasha nan take da kuma goyon bayan kaddamar da tattaunawar zaman lafiya a karkashin kungiyar Tarayyar Afirka ta  AU, a cewar ma’aikatar harkokin wajen Amurka.

A farkon watan Oktoba ne gwamnatin tarayya ta Firaminista Abiy Ahmed da wakilan ‘yan tawaye a yankin Tigray suka ce a shirye suke su je tattaunawar da kungiyar kasashen afirka ta AU ta gayyace su a Afirka ta Kudu.

Sai dai ba a iya gudanar da wannan tattaunawa ba, musamman saboda matsalolin kungiyoyi da na kayan aiki, a cewar jami’an diflomasiyya.

A ranar Juma’a, yayin tattaunawa da  Hammer,  firaministan kasar Habasha Demeke wanda kuma shi ne ministan harkokin wajen kasar, ya ​​jaddada aniyar gwamnati na ganin an warware rikicin arewacin kasar cikin lumana”, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta wallafa a shafinta na twitter.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp