Home DUNIYA Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon...

Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon kanaki 3 – Blinken

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya ce janar-janar da ke rikici a Sudan sun amince sun tsagaita wuta ta kwana uku ranar Litinin, bayan an kwashe kwana 10 ana fafatawa tsakaninsu.

Yarjejeniyoyin tsagaita wutar da suka kulla a baya ba su yi tasiri ba lamarin da ya kai ga kisan daruruwan mutane da kuma raba dubbai daga gidajensu.

Sai dai Blinken ya ce “bayan an kwashe sama da awa 48 ana tattaunawa sosai, Rundunar Sojin Sudan da Rapid Support Forces (RSF) sun amince su aiwatar da jarjejeniyar tsagaita wuta ta awa 72 daga ranar Litinin da daddare.”

Sakataren Wajen Amurka ya yi kalaman ne awa biyu kafin a soma aiwatar da yarjejeniyar.

Hakan na faruwa ne a lokacin da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadin cewa Sudan na “dab da fadawa cikin bala’i” sakamakon rikici tsakanin bangarorin biyu, wadanda ke fafatawa a Khartoum da wasu bangarori na kasar.

An kashe akalla mutum 427 yayin da fiye da mutum 3,700 suka jikkata sakamakon rikicin, a cewar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya.

Wani babban jami’in ofishin jakadancin Masar a Khartoum yana cikin wadanda aka kashe a baya bayan nan, a cewar ma’aikatar wajen kasar.

An kashe shi ne yayin da yake kan hanyar zuwa ofishin jakadancin domin sanin halin da ake ciki game da yiwuwar kwashe su daga Sudan.

Rikicin na faruwa ne tsakanin runsunar sojin da ke karkashin Janar Abdel Fattah al Burhan da dakarun RSF da ke karkashin tsohon mataimakinsa Janar Mohamed Hamdan Dagalo.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp