Home DUNIYA Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon...

Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon kanaki 3 – Blinken

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya ce janar-janar da ke rikici a Sudan sun amince sun tsagaita wuta ta kwana uku ranar Litinin, bayan an kwashe kwana 10 ana fafatawa tsakaninsu.

Yarjejeniyoyin tsagaita wutar da suka kulla a baya ba su yi tasiri ba lamarin da ya kai ga kisan daruruwan mutane da kuma raba dubbai daga gidajensu.

Sai dai Blinken ya ce “bayan an kwashe sama da awa 48 ana tattaunawa sosai, Rundunar Sojin Sudan da Rapid Support Forces (RSF) sun amince su aiwatar da jarjejeniyar tsagaita wuta ta awa 72 daga ranar Litinin da daddare.”

Sakataren Wajen Amurka ya yi kalaman ne awa biyu kafin a soma aiwatar da yarjejeniyar.

Hakan na faruwa ne a lokacin da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadin cewa Sudan na “dab da fadawa cikin bala’i” sakamakon rikici tsakanin bangarorin biyu, wadanda ke fafatawa a Khartoum da wasu bangarori na kasar.

An kashe akalla mutum 427 yayin da fiye da mutum 3,700 suka jikkata sakamakon rikicin, a cewar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya.

Wani babban jami’in ofishin jakadancin Masar a Khartoum yana cikin wadanda aka kashe a baya bayan nan, a cewar ma’aikatar wajen kasar.

An kashe shi ne yayin da yake kan hanyar zuwa ofishin jakadancin domin sanin halin da ake ciki game da yiwuwar kwashe su daga Sudan.

Rikicin na faruwa ne tsakanin runsunar sojin da ke karkashin Janar Abdel Fattah al Burhan da dakarun RSF da ke karkashin tsohon mataimakinsa Janar Mohamed Hamdan Dagalo.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp