Home Labarai Sojojin Nijeriya sun bankado maboyar mayakan ISWAP a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun bankado maboyar mayakan ISWAP a jihar Borno

Rundunar sojojin Najeriya ta ce dakarunta sun sami nasarar bankado maboyar mayakan boko haram tsagin ISWAP a jihar Borno dake Arewa maso gabashin kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Onyema Nwachukwa ya fitar aka raba manema labarai.

Sanarwar ta ce dakarun rundunar karkashin “operation Desert Sanity III” sun kai wani harin ta sama da kuma makaman atilare a hannu guda da wasu dakru na musamman a kauyukan Ngumne, kawaran da Mangu dake dajin sambisa da yankin Timbuktu.

Yace dakarun sojin sun yi bata-kashi da mayakan boko haram inda suka yi amfani da wasu makamai masu fashewa kan mayakan na ISWAP, wannan ta sanya suka ci karfin mayakan inda suka ranta a na kare.

Nwachukwa ya kara da cewa dakarun sojin sun sami nasarar kwato manyan makamai, da suka hadar da motar dake daukan bindigu, bindigar kirar 105mm howitzer, haka kuma sun tarwatsa maboyar mayakan na ISWAP.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp