Home General Bama-baman Lakurawa ne suka kashe mutane a Sokoto ba sojoji ba –...

Bama-baman Lakurawa ne suka kashe mutane a Sokoto ba sojoji ba – Sojin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce bama-baman da Lakurawa suka ajiye a ƙauyukan da sojojin suka kai wa hari ne suka kashe mutanen gari, ba hare-haren da sojojin suka ƙaddamar ba.

Cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron Najeriyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaranta, Manjo Janar Edwar Buba ta ce ba harin sojojin ne ya kashe mutanen ba.

Jami’in ya ce kafin kai harin, sai da sojojin suka ɗauki tsawon lokaci suna gudanar da bincike ta hanyar tattara bayanan sirri, kuma sai da suka tabbatar da cewa Lakurawa ne ke kai kawo a yankin kafin afka musu.

A ranar Laraba ne aka samu rahotonnin hare-haren jiragen sojin Najeriya a wasu ƙauyuka biyu da ke yankin ƙaramar hukumar Silame a jihar Sokoto.

Gwamnan jihar, Ahmad Aliyu ya ce sojojin ƙasar ne suka kai harin bisa kuskure, lamarin ya yi sanadin mutuwar mutune 10.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp