Home General Bamu Fara daukan sabbin Ma’aikata ba- KAROTA

Bamu Fara daukan sabbin Ma’aikata ba- KAROTA

Hukumar Kula da Zirga- zirgar Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA ta musanta jita-jitar da ake yadawa na fara daukar aiki a Hukumar.

Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka a ranar lahadi, ta bakin mai magana da yawun Hukumar Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa inda Yace Babu gaskiya a batun daukar Sabbin Ma’aikata.

Nabilusi Kofar Na’isa Ya ce Hukumar ta lura da jita-jitar da ake yadawa na fara daukar sabbin Jami’an Hukumar wadanda hakan ba gaskiya ba ne kwata-kwata.

Sai dai Kuma sanarwar tace Hukumar na tsaka da aikin tantance daukacin Jami’an KAROTA domin duba yuiwuwar daukar sabbi.

A don haka Hukumar ke gargadin jama’a, da su guji yada jita-jitar fara daukar sabbin Jami’an na Hukumar ta KAROTA

Hukumar ta ce duk wanda ta kama da hannu wajen yada jita-jitar zata dauki matakin sharia a kansa.

Engr. Faisal ya roki jama’a da su yi gaggawar sanar da Hukumar ta KAROTA ko ofishin ‘Yansanda mafi kusa wanda duk aka samu yana yada jita-jitar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp