Home Labarai Sojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi...

Sojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Najeriya ta bakin kakakin ma’aikatar tsaronta ta tabbatar da isowar sojojin Amurka aƙalla 100 cikin ƙasar ta yammacin Afrika don taimaka mata a yaƙin da ta ke da ƴan ta’addar da ke kaiwa jama’a hare-hare.

Kakakin shalkwatar tsaron Najeriyar Manjo Janar Samaila Uba ya ce tabbas sojojin Amurkan sun shiga Najeriyar amma ba za su shiga fagen daga don yin yaƙi ba, face aikin horar da dakarun Najeriyar dabarun yaƙi da ƴan ta’addan.

Isowar sojojin Amurka na zuwa bayan tun farko Donald Trump ya zargi Najeriyar da gazawa wajen baiwa Kiristoci kariya daga hare-haren da ƴanta’addan da ya kira da Musulmai ke kaiwa a sassan ƙasar.

Sai dai tuni gwamnatin Najeriya ta musanta wannan zargin bayan da ta ce ƴan ta’addan na kashe dukkanin ɓangarorin Musulmai da kuma Kiristoci kuma dakarunta na aiki tuƙuru wajen yaƙi da su musamman a yankin arewa maso yammaci da kuma arewa maso gabas.

Amurkan ta kai hare-hare cikin watan Disamba kan yankunan da ta ce a nan ne mayaƙan IS suke a yankin na arewa maso yammacin Najeriyar kuma tun daga wancan lokaci bayanai ke cewa akwai sojojin na Washington da jiragen yaƙinta da ke shawagi a sassan Najeriyar don yaƙi da matsalolin tsaron.

Cikin kwanakin baya-bayan nan anga tarin jiragen yaƙin Amurka ɗauke da ko dai sojoji ko kuma makamai na isa sassan jihohin arewacin ƙasar kamar yadda bayanan bin diddigin da kafar Reuters ke yi suka bayyana.

Tun a farkon watan nan ma’aikatar tsaron Najeriyar ta ce tana tsammanin isowar ƙarin Sojin Amurka 200 zuwa ƙasar.

Najeriya mai yawan jama’a fiye da miliyan 240 na da rinjaye mabiyan addinin Islama ne a yankin arewaci yayinda mabiya addinin Kirista ke a yankin kudanci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp