Gwamnan Kwara ya yi Magana Kan Sanya Hijabi Cikin Makarantun Jahar

Gwamnan Kwara ya yi Magana Kan Sanya Hijabi Cikin Makarantun Jahar

Gwamnan jahar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya bayyana cewa ko shakka babu yana tare da dalibai mata Musulmai kan lamarin sanya Hijabi cikin makarantun jahar.

Yace wannan ita ce matsayarsa saboda shari’o’in da kotu ta yanke kan lamarin da kuma kasancewar Kwara jaha mai daidaito tsakanin addinai kuma jahar da tafi kama da kudu wajen adadin masu addinai mabananta.

Abdulrazaq yace gwamnatinsa kawai doka da gaskiya take bi da kuma nuna adalci tsakanin kowa, sakataren yada labaransa, Rafiu Ajakaye, ya bayyana, rahoton Daily Trust.

Wannan jawabi na Gwamna ya biyo bayan tuhume-tuhumen da Musulmai da Kirista ke yi cewa Gwamnan ya ki bayyana ra’ayinsa kan lamarin saboda siyasa.

Tuni dai iyalan Habeeb Idris, dalibin da aka kashe yayin zanga-zanga a makarantar Oyun Baptsit kwanakin baya sun yi watsi da diyyar N1m da gwamnatin jahar ta basu.

Hakazalika mutum 11 da suka jikkata sun yi watsi da kudi N250,000 da gwamnatin jahar ta basu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 35 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 16 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here