Home SIYASA Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga...

Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga Mulki

Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga Mulki

Gwamnan jahar Ebonyi David Umahi da ke kudu maso gabashin Najeriya ya daukaka kara game da hukuncin wata babbar kotun tarayya wadda ta bayar da umurnin sauke shi daga mulki bisa sauya sheka da ya yi daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Takardar da suka gabatar ta daukaka karar, ta ce kotun ta yi kuskure a hukuncin da ta yanke, saboda haka ne ya ce yana da ja da daukacin shari’ar.

Takardar ta ce kotun ta gaza bisa dogaron da ta yi da sashen na 68, da na 109 na kundin tsarin Mulki wanda dole gwamnan ya bar mukaminsa kasancewar ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP wadda aka zabe shi a karkashinta, zuwa jam’iyyar APC mai mulkin kasar, wanda hakan a cewar takardar tamkar watsi ne da wani hukunci da kotun kolin kasar ta taba yankewa, tsakanin ministan shari’a na Najeriya da tsohon mataimakain shugaban kasa Atiku Abubakar, inda ta ce babu wani tanadin kundin tsarin mulki da ya haramta wa shugaban kasa, ko mataimakinsa, ko kuma gwamnan, ko mataimakinsa daga sauya sheka daga wata jam’iyya zuwa wata.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp