Home SIYASA Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba...

Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba Shehu

Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba Shehu

 

Ga alama batun zaɓen shugaban APC ta hanyar maslaha zai yi wuya, inda wasu ƴan takara har zuwa ranar babban taron jam’iyyar ba su janye ba.

Jam’iyyar APC dai ta nuna cewa tsarin daidaitawa ko maslaha ne tsarin da ta fi so wajen zaɓar shugabanninta.

Shugaba Buhari ma ya nuna tsarin maslaha ko daidaitawa tsakanin ƴan takara ne yake goyon baya.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Malam Garba Shehu, kuma jami`i a kwamitin yada labarai na babban taron APC ya ce maslaha za a bai wa fifiko, kuma abin da jiga-jigan APC suka kashe dare suna yi ke nan, suna lallashin sauran `yan takara domin su mara wa mutum guda. Har ma an ba da umurnin jam`iyya ta mayar musu da kudin da suka kashe wajen sayen fam.

Mutum tara ne suka nuna sha`awar takarar shugabancin jam`iyyar, kuma har zuwa safiyar Asabar ranar babban taron APC babu labarin janyewar wasu ƴan takarar da ke neman shugabancin jam’iyyar.

Tun tuni rahotanni ke cewa tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Senata Abdullahi Adamu ne shugban kasa da jiga-jigan APC ke goyon baya don zama shugaban jam`iyya, kuma har yanzu fadar shugaban kasa ba ta musanta ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp