Home General Rundunar Sojin Najeriya ta Dukufa Wajen Bankado Jami’in Ta da Ya Bata.

Rundunar Sojin Najeriya ta Dukufa Wajen Bankado Jami’in Ta da Ya Bata.

Rundunar Sojin Nijeriya tace ta dukufa wajen bankadowa tare da tseratar da kwamandan sojan da yayi batan dabo yayin gudanar da atisayen kawar da ‘yan ta’adda a jihar Taraba.

Wannan nakunshe ne ta cikin wata takarda mai dauke da sahannun Daraktan yada labaran Rundunar Birgediya Janar Onyema Nwachukwu.

Dakarun dai sun sami kiran waya dake tabbatar da cewa kauyen na Tati na fuskantar harin ‘yan bindiga, sai dai a kokarin sun a fatattakar ‘yan ta’addar suka fada komar su, inda sojoji 6 suka kwanta dama, yayin da babban jami’in soji guda ya bata.

Sai dai Rundunar hadin Gwuiwa ta dakarun sojin da suka kai dauki kauyen Ananum dake karamar hukumar Donga ta jihar, sun hallaka ‘yan bindiga 2 tare da kwato bindiga kirar Ak 47 guda daya, bindiga kirar gida guda daya alburusai masu tsayin 19.7.62mm na musamman baburan hawa guda 3 dai dai sauran muggana makamai.

A halin yanzu dai dakarun sojin na cigaba da bincikar sojojin da suka bata tare da kokarin bankado da maboyar ‘yan ta’addan.

Idan dai za’a iya tunawa Jaridar PRNigeria Hausa ta rawaito cewa dakarun rundunar Sojin bataliya ta 93 sun yi batan dabo, tun bayan suka kai wani sumamen aiki ga maboyar ‘Yan Ta’adda a kauyen Tati dake karamar hukuma Takum ta Jihar Taraba a yammacin Talata.

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp