Gobara :Fashewar Gas Ta Yi Sanadiyyar Jakkatar Mutane 20 a Jihar Kano

Wasu rahotannin daga jihar Kano sun tabbatar da sake samun fashewa a shagon sayar da gas ɗin girki a wata unguwa da ke cikin garin Kano, lamarin da ya jikkata mutum 20 da ƙona shaguna da dama.

Ko da yake dai wannan adadi na mutum 20 ganau ne suka tabbatarwa da PRNigeria ba hukumomin da abun ya shafa ba, duk da cewa wani bayani ya tabbatar da cewa jami’an tsaro a jihar na ganawa yanzu haka kan lamarin.

Wannan dai na zuwa ne makwanni bayan samun irin wannan fashewar a titin Aba dake unguwar Sabon Gari a Kano, inda mutum 9 da suka mutu baya ga wadanda suka jikkata.

Ko da yake a wannan lokacin an yi ta samun bayanai masu cin karo da juna, rundunar ‘yan sanda na cewa tukunyar gas ce, ganau kuma na cewa bam ne. duk da cewa daga bisani rundunar ‘yan sanda ta fito ta bayyana cewa wani mai sayar da kayan hada bam ne ya tashi da shi.

Rahotanni dai na cewa iftila’in na wannan lokaci ya faru ne a unguwar Sheka, Karshen-Kwalta.

Sai dai ganau sun ce mutum guda ya rigamu gidan gaskiya

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 10 minutes 16 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 51 minutes 41 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com