Home General Gobara :Fashewar Gas Ta Yi Sanadiyyar Jakkatar Mutane 20 a Jihar Kano

Gobara :Fashewar Gas Ta Yi Sanadiyyar Jakkatar Mutane 20 a Jihar Kano

Wasu rahotannin daga jihar Kano sun tabbatar da sake samun fashewa a shagon sayar da gas ɗin girki a wata unguwa da ke cikin garin Kano, lamarin da ya jikkata mutum 20 da ƙona shaguna da dama.

Ko da yake dai wannan adadi na mutum 20 ganau ne suka tabbatarwa da PRNigeria ba hukumomin da abun ya shafa ba, duk da cewa wani bayani ya tabbatar da cewa jami’an tsaro a jihar na ganawa yanzu haka kan lamarin.

Wannan dai na zuwa ne makwanni bayan samun irin wannan fashewar a titin Aba dake unguwar Sabon Gari a Kano, inda mutum 9 da suka mutu baya ga wadanda suka jikkata.

Ko da yake a wannan lokacin an yi ta samun bayanai masu cin karo da juna, rundunar ‘yan sanda na cewa tukunyar gas ce, ganau kuma na cewa bam ne. duk da cewa daga bisani rundunar ‘yan sanda ta fito ta bayyana cewa wani mai sayar da kayan hada bam ne ya tashi da shi.

Rahotanni dai na cewa iftila’in na wannan lokaci ya faru ne a unguwar Sheka, Karshen-Kwalta.

Sai dai ganau sun ce mutum guda ya rigamu gidan gaskiya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp