Home SIYASA Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar...

Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar Ministoci

Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar Ministoci

 

By Ozumi Abdul-Satumba 7, 2022

Kemi Badenoch

LABARIN SIYASA- Sabuwar Firaministan Burtaniya, Liz Truss ta nada wata ‘yar siyasa ‘yar asalin Najeriya, Kemi Badenoch, a matsayin mamba a sabuwar majalisar ministocinta da aka yi wa garambawul a ranar Talata.

An nada Kemi a matsayin sabuwar sakatariyar kasuwancin kasa da kasa kuma shugabar hukumar kasuwanci.

Nadin, wanda ke kunshe a cikin wani sakon twitter da aka buga a tabbataccen shafin Twitter na Firayim Ministan Burtaniya, @10DowningStreet ranar Talata ya karanta:

“An nada Kemi Badenoch MP @KemiBadenoch Sakatariyar Harkokin Ciniki ta Kasa da Kasa kuma Shugabar Hukumar Kasuwanci @TradeGovUK.”

Da take amincewa da nadin, Kemi ta yi amfani da tabbataccen shafinta na Twitter inda ta bayyana jin dadin ta da nadin.

Babbar mamba ta jam’iyyar Conservative ta ce ba za ta iya jira ta yi cikakken amfani da damar Biritaniya don samar da karin ayyuka da damammaki ba.

“Na yi farin cikin fara sabon aiki na a @tradegovuk! Muna sa ran fitar da cikakken damar Duniyar Burtaniya ta yadda za mu iya samar da karin ayyukan yi, karin ci gaba da karin damammaki a fadin Burtaniya, ”in ji ta.

A baya Kemi Badenoch ta taba rike mukamin karamar ministar kananan hukumomi da imani da al’ummomi da kuma karamar ministar daidaito.

Kemi Badenoch, wacce ita ma ta tsaya takarar shugaban jam’iyyar Conservative, Rishi Sunak, Penny Mordaunt, da Liz Truss, da ta lashe zaben, ta fice daga takarar neman zama sabon Firaminista.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp