Home SIYASA PDP: Ayu ya Mika wa Mataimakin sa Shugabancin Jam’iyyar

PDP: Ayu ya Mika wa Mataimakin sa Shugabancin Jam’iyyar

PDP: Ayu ya Mika wa Mataimakin sa Shugabancin Jam’iyyar

 

Daga Ozumi Abdul

SIYASA – Shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) na kasa, Dr. Iyorchia Ayu, ya tashi daga kasar zuwa Turai, yayin da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya kara jaddada kiransa na yin murabus.

Ayu ya mikawa mataimakin shugaban jam’iyyar (Arewa), Iliya Damagun, wanda zai ci gaba da tafiyar da jam’iyyar a matsayin shugaban riko.

Wannan na zuwa ne a wata sanarwa da mai ba da shawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa na Ayu, Simon Imobo-Tswam, ya fitar a ranar Talata.

Sanarwar ta ce: “Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Dr. Iyorchia Ayu, zai bar Najeriya zuwa Turai gobe Laraba.

“Ayu zai yi waje da kasar na kusan makonni biyu. Yayin da ya tafi, Mataimakin Shugaban (Arewa), Iliya Damagun, zai yi aiki a madadinsa.

“Tuni shugaban kasa ya mika takardar mika mulki ga hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta.

Ana sa ran zai dawo a karshen wata.”

Gwamna Wike da sansaninsa a cikin jam’iyyar PDP sun yi ta kiraye-kirayen murabus din Ayu bisa ga alkawarin da ya yi wa ‘yan jam’iyyar na cewa idan dan Arewa ya fito takarar shugaban kasa zai yi murabus.

Sai dai a kwanakin baya Ayu ya ce ba zai sauka ba, yana mai cewa irin su Wike da ke kiran kan sa yara ne da ba su nan a lokacin da aka kafa jam’iyyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp