Home General ‘Yan Bindiga: An Ceto Sauran Fasinjojin Jirgin Kaduna zuwa Abuja da Suka...

‘Yan Bindiga: An Ceto Sauran Fasinjojin Jirgin Kaduna zuwa Abuja da Suka Rage Hannun ‘Yan Fashin Daji

Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa An sako dukkan fasinjojin da suka rage a hannun wadanda ke garkuwa da su bayan da aka sace su a watan Maris na shekarar 2022 a cikin wani jirgin kasan da ke kan hanyar zuwa Kaduna daga birnin tarayya Abuja.
Wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa da gwamnatin kasar ta fitar ta hannun sakataren wani kwamitin ma’aikatar tsaron Najeriya CDSAC Farfesa Usman Yusuf ya fitar a ranar ranar Laraba, wadda take da yammacin ranar laraba dakarun soji sun sami nasarar ce sauran mutane da suka rage hannun masu garkuwar.
“Ina mai farin cikin sanar da kasa da ma duniya cewa da misalin karfe 4 na yammacin yau Laraba 5 ga watan Oktoba 2022, kwamitin mutum bakwai da hafsan hafsoshin dakarun tsaron kasa Janar L. E. O. Irabor ya sami nasarar ceto sauran fasinjoji 23 da suka rage a hannun ‘yan ta’adda na Boko Haram bayan da suka kai hari kan jirgin kasan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna ranar 28 ga watan Maris na 2022.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan kasar na cike da godiya ga sojojin Najeriya a karkashin jagorancin hafsan hafsoshin sojojin kasar, wanda shi ne ya jagoranci aikin daga farkonsa har zuwa karshe. Haka ma, sauran hukumomin tsaro da ma’aikatar sufuri duka sun taimaka gaya wajen nasarar da muka samu a wannan aikin.”
Sai dai kawo yanzu babu rahotannin inda aka kai fasinjojin da aka sako, ko yadda aka iya karbo su daga hannun ‘yan Boko Haram din da suka yi garkuwa da su na tsawon fiye da wata shida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp