Home General ASUU ta Janye Yajin Aiki da Take Tsawon Watannin 8

ASUU ta Janye Yajin Aiki da Take Tsawon Watannin 8

Kungiyar malaman Jami’oin Nijeriya ta (ASUU) ta dakatar da yajin aikin data kwashe tsawon watannin ta yi bisa wasu dalilai, kamar yadda kwamitin amintattun kungiyar ya shaidawa manema labarai a safiyar juma’a.

Kungiyar ta yanke hukuncin janye yajin aikin ne bayan wata ganawa da shuwagabannin suka fara gudanarwa tun daga daren alhamis zuwa wayewar garin juma’a.

Kungiyar ta kira taron gawanar ne domin yanke matakin ta na karshe bayan da mambobin ta na jihohi suka gana kan hukuncin kotun daukaka kara a makon daya gabata.

Kotun daukaka kara ta umarci kungiyar ASUU da ta dakatar da yajin aikin kafin a saurari daukaka karar da ta yanke, inda ta umarci malam su koma bakin aiki.

Mambobin kwamitin zartawa na kungiyar na kasa, wadanda suka hadar da shuwagabannin kungiyar na jihohin dana kasa ne suka halarci taron a sakatariyar kungiyar ta ASUU dake birnin tarayya Abuja.

Kungiyar malaman jami’oin ta ASUU ta tsunduma yajin aikin ne tun a 14 ga watan fabrerun 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp