Home DUNIYA Ana Zanga-Zanga kan Tabarbarewar Tattalin Arziki A Tunisia

Ana Zanga-Zanga kan Tabarbarewar Tattalin Arziki A Tunisia

Dubu Dubatar ‘yan kasar Tunisiya ne suka gudanar da zanga-zanga a birnin Tunis a jiya asabar don yin tir da manufofin shugaba Kais Sa’id, wanda suke zargin shi ne ke da alhakin tabarbarewar tattalin arzikin kasar, wanda ke fuskantar matsalar karancin kayan masarufi da hauhawar farashin kayayyaki.

A karkashin jagorancin jam’iyyar National Salvation Front, gamayyar jam’iyyun adawa masu zanga-zangar sun tsallaka manyan titunan babban birnin Tunisiya, suna kira da shugaban ya yi murabus.

Wannan zanga-zangar tana nuna fushin halin da ake ciki a Tunisiya karkashin Kais Saied da kuma kira da  ya yi murabus, kamar yada tsohon Fira Minista Ali Laaraydh, mataimakin shugaban Ennahdha, ya shaida wa manema labarai.

A dai-dai lokacin da jama’a ke gudanar da wannan zanga-zanga ,asusun ba da lamuni na duniya IMF ya cimma yarjejeniya da gwamnatin kasar ta Tunisia wadda za ta bada damar biyan dala biliyan 1.9 yayin da Tunisia ke fama da matsananciyar matsalar tattalin arziki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp