Home DUNIYA Harin Al-Shabab yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 9 tare da Jikkata 47 a...

Harin Al-Shabab yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 9 tare da Jikkata 47 a Somalia

Rahotanni na bayyana cewa Akalla mutane 9 aka kashe, tare da jikkata wasu 47 sakamakon harin kan wani Otal da ke birnin Kismaayo a kudancin Somalia, farmakin da kungiyar Al-Shabaab ta dauki alhakinsa a ranar Lahadi.

Birnin na Kisimaayo mai tashar jiragen ruwa shi ne na baya-bayan nan da ya fuskanci hare-haren kungiyar Al Shebaab mai alaka da Al-Qaeda, wadda ta fi mayar da hankali wajen kai hare-hare a birnin Mogadishu da kuma yankin tsakiyar kasar Somalia.

Bayanai sun ce, mayakan na Al Sheebaab sun kaddamar da harin na ranar Lahadi ne da misalin karfe 12:45 na rana wato 9:45 na safe agogon GMT, lokacin da wata mota makare da bama-bamai ta afkawa kofar shiga Otal din Tawakal. Sai kuma da aka shafe sa’o’i shidda kafin jami’an tsaro su kashe mahara uku da suka kai farmakin, yayin da ragowar guda ya tarwatsa damarar bam din da ke jikinsa.

Ministan tsaron yankin Jubaland Yusuf Hussein Osman ya shaida wa manema labarai cewa, daga cikin wadanda suka jikkata a harin akwai daliban da suka tashi daga wata makaranta da ke kusa da inda aka kai farmakin.

‘Yan sandan Somalia sun ce fararen hula ne suka fi mu’amala da Otal din da aka kaiwa hari, sai dai kungiyar Al-Shabaab ta ce mambobin gwamnatin yankin Jubaland, inda birnin Kismayo yake, suna ganawa cikin Otal din, a lokacin da mayakanta suka kai farmakin na sa’o’i 6.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp