Home DUNIYA Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Watanni biyu bayan samun nasarar lashe zaben shugaban kasar Kenya William Ruto ya rantsar da kunshin majalisar ministocin a ranar Alhamis.

Ministocin guda 12 an rantsar dasu ne domin tunkarar matsalolin da suka addabi kasar da suka hada da tsadar rayuwa da kuma sauran batutuwa suka shafi tattalin Arziki a kasar dake gabashin nahiyar Afirka, wanda wannan na cikin alkawurran da Ruto ya dauka yayin yakin neman zaben sa.

Sai dai kuma ana kallon sabuwar majalisar da Ruto ya kafa bata cimma daidaiton jinsi ba kamar yadda ya alkawurta tun a yakin neman zaben nasa, inda aka bayyana sunayen mata 7 kawai.

Tsohon mataimakain shugaban kasar kuma tsohon dan adawar Raila Odinga daya marawa Ruto baya Musalia Mudavadi ya zama sabon sakataren firaministan kasar da aka kirkiro.

Sai kuma Alfred tsohon gwamna wanda jam’iyyar sa ta goyi bayan Ruto shi ne zai jagoranci ma’aikatar harkokin wajen kasar.

Kithure Kindiki, wand ana cikin lauyoyin da suka kare zaben Ruto a watan Agusta, shine zai jagoranci ma’aikatar cikin gida mai karfi.

Kindiki shine wanda ya wakilci Ruto a shari’ar da ake yi masa a Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa dake birnin Hague lokacin da aka zrge shi da hannu wajen kitsa tarzomar da ta biyo bayan zaben 2007- 2008 wanda yayi sanadin mutuwar mutane akall 1,100 tare da raba sama da 600,000 da muhallansu.

Sai kuma ma’ajin kasar da Njuguna Ndung’u zai jagoranta, wanda shine tsohon gwamnan babban bankin kasar.

 PRNigeria Hausa

(AFRICA NEWS)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp