Home DUNIYA Wani Farmakin Hadin Gwiwa tsakano Congo da Burundi ya halaka mayaka 40

Wani Farmakin Hadin Gwiwa tsakano Congo da Burundi ya halaka mayaka 40

Rahotannin na bayyana An halaka ‘yan tawayen Burundi 40 a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo da Burundi suka kai a gabashin Congo.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Laftanar Marc Elongo-Kyondwa ya ce sojojin biyu “sun kai wani gagarumin farmaki” kan ‘yan tawayen Burundi.

Ya kara da cewa sojojin biyu sun fatattaki ‘yan tawayen FNL daga dukkan tsaunuka hudu da ke yankin Nabombi.

Sanarwar ta ruwaito Janar Ramazani Fundi, kwamandan ayyuka a yankin kudancin kasar Congo yana cewa, rundunar sojojin Congon ta yi kira ga al’ummar yankin da su ba da hadin kai ga sojojin, sannan kuma matasa su ware kansu daga kungiyoyin da ke dauke da makamai”.

Tun a watan Agusta, sojojin Burundin ke yaki da kungiyoyin masu dauke da makamai a yankin Kivu ta Kudu, a matsayin wani bangare na rundunar kungiyar kasashen gabashin Afirka (EAC).

A cikin watan Yuni, EAC ta yanke shawarar kafa rundunar yankin da ta kunshi sojojin Kenya da Uganda tare da sojojin Congo a arewacin Kivu da Ituri, da sojojin Sudan ta Kudu da ke Haut-Uele da kuma Burundi a kudancin Kivu.

Kinshasa da ke zargin Rwanda da goyon bayan ‘yan tawayen M23 a arewacin Kivu, ta ki yarda Kigali ta shiga cikin rundunar.

Kimanin shekaru 30 kenan gabashin Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ke fama da kungiyoyin masu dauke da makamai, wasu na cikin gida, wasu kuma daga kasashe makwabta.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp