Home General Hukumar EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade...

Hukumar EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a kasar

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a jahohin kasar 12 da aka kwace daga wajen wadanda aka zarga da cin hanci da rashawa.
Mai magana da yawun hukumar ta EFCC Wilson Uwujaren ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, babban birnin kasar.
Tuni dai wasu suka fara kiran gudanar da bincike wajen gano sahihancin kudaden wadanda za’a sake saida wa irin wadan nan kaddarori.
A bayan bayan nan ne rahotanni daga Najeriya ke cewa EFCC za ta yi gwanjon gidaje da filaye 144 da aka kwace a fadin kasar, inda jihohin Legas, Abuja da kuma Jihar Ribas ke kan gaba.
Kakakin EFCC ya bayyana cewa daga cikin kadadrorin, akwai gidaje 24 da ke rukunin gidaje na Banana Island, sai 21 a Thornburn, Yaba, duka a Legas,sai kuma 6 na a Court Estate da ke birnin Fatakwal.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp