Hukumar EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a kasar

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a jahohin kasar 12 da aka kwace daga wajen wadanda aka zarga da cin hanci da rashawa.
Mai magana da yawun hukumar ta EFCC Wilson Uwujaren ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, babban birnin kasar.
Tuni dai wasu suka fara kiran gudanar da bincike wajen gano sahihancin kudaden wadanda za’a sake saida wa irin wadan nan kaddarori.
A bayan bayan nan ne rahotanni daga Najeriya ke cewa EFCC za ta yi gwanjon gidaje da filaye 144 da aka kwace a fadin kasar, inda jihohin Legas, Abuja da kuma Jihar Ribas ke kan gaba.
Kakakin EFCC ya bayyana cewa daga cikin kadadrorin, akwai gidaje 24 da ke rukunin gidaje na Banana Island, sai 21 a Thornburn, Yaba, duka a Legas,sai kuma 6 na a Court Estate da ke birnin Fatakwal.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 29 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 10 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com