Home General Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn...

Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn tare da sabbin masu zuba jari duk shekara.

Shugaban Nijeriya Muhammad Buhari yace kamfanin samar da karafa na Ajakuta zai ke samar da dala biliyan 1.6 dukkan shekara tare da samar da guraban ayyuka ga matasan kasar.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Mai Magana da yawun shugaban kasar Malam garba shehu ya fitar, wadda tace shugaban kasar ya bayyana hakan ne a fadar ohinoyi na garin Ebira, wanda kuma ya kaddamar da ziyarar aiki ta kwana guda a garin Okene na jihar kogi ranar Alhamis.
Shehu ya bayyana cewa Buhari ya magantu kan kudirin gwamnatin sa na mayar da jihar kogi matsayin cibiyar masana’antu kuma jihar da zata zama wajen samar da albakatun kasa.
Shugaban ya bayyana yadda gwamantin tarayya ta cimma matsaya kan dukkan wata doka da zata kawo tasgaro ga ciban kamfanin samar da karafan na Ajaokuta.
Inda yace aikin zai matukar amfanar da Al’ummar jihar
Shugaban y ace jihar kogi za kuma ta ci gajiyar aikin ta hanyoyi daban-daban musamman idan bututun iskar gas na AKK daya ratsa ta cikin jihar mai tsawon kilmita 614 (mil 384) wanda ake sa ran fara aikin sa a shekarar 2023.
Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar sa ta APC ta cika dukkan Alkawuran data daukarwa Al’ummar Nijeriya a ko wanne mataki.
Daga bisa ya bayyana cewa gwamnan jihar Yahaya Bello yayi abin a yaba a lokacin mulkinsa na tsahon shekaru 8 wato zango biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp