Home General TCN zata ruguje gidaje dubu 1 a jihar kano

TCN zata ruguje gidaje dubu 1 a jihar kano

Kamfanin dakon wutar lantarki na Nijeriya (TCN) ya bayyana cewa babu gudu ba ja da baya kan yunkurin s ana ruguje gidaje dubu 1 da aka gin aba bisa ka’ida ba karkashi turakun wayoyin lanatarki a jihar kano.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke musanta cewa gidajen da aka ware domin rugujewa sun haura dubu 20, inda kamfanin yace tun daga dan’agundi zuwa kumbotso gidaje da gine-gine da ba kamala ba basu wuce 100 ba.
Mataimakin Babban daraktan kamfanin, Alh. Muhammad Kamaru Bello, yace layin wayar wutar lantarki guda daya ne ya kawo wuta jihar kano daga jihar Kaduna wanda kuma aka hada shi tsahon shekaru 50 da suka gabata.
Sai dai mafi yawa daga cikin su an gaza biyan su hakkokin su, kuma hakn ya biyo bayan biyan daiyyar naira biliyan 1.5 yayin da kano ta biya naira miliyan 500 a tashar wutar ta Dan’Agundi da tashar rimin zakara.
Yace tashar wutar ta Dan’aAgundi an samar da ita ne shekaru hamsim da suka gabata, wadda take bada megawatts 80, amma zuwa yamzun tana samar da sama da megawatt 280 wannan ne ya sanya za’a gudanar da aikin.
Ya bayyana cewa dukkan wasu shirye-shirye wajen gudanar da aikin nan da kwanaki masu zuwa, za’a fara aikin sake gina layukan samar da wutar lantarki na biyu daga kano zuwa kaduna, yace babu gudu babu ja da baya.
PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristociTinubu ya tura bataliyar soji jihar KwaraGwamnatin Kogi ta ba da umarnin rufe makarantun firamare da na sakandare a jiharNNPCL zai dauko ƙwararru daga chaina domin inganta Matatun kasarMajalisar dattijai ta amince da kudirin dokar zaɓen da aka yi wa gyaran fuskaGwamnatin Kano ta fara kwashe masu larurar ƙwaƙwalwa daga titunan jiharKotu ta hana ƙungiyoyin ƙwadago yin yajin aiki ko zanga-zangaBabu gudu ba ja da baya kan zanga-zanga a Abuja - NLC
X whatsapp