Buhari ya gargadi masu shirin kawo cikas a zaben 2023

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya yi gargadi wadanda ke kokarin kawo cikas ga zabukan da ake shirin gudanarwa cikin shekara ta 2023 a kasar cewa lalle za su hadu da fushin doka.
Shugaba Buhari ya yi wannan gargadi ne a jawabin da ya gabatar wa al’ummar kasar dangane da shiga sabuwar shekara ta 2023, yana mai kira ga illahirin ‘yan Najeriya da su tabbatar da wadannan zabuka sun gudana a cikin yanayi na tsari, ‘yanci da kuma mutunta doka.
Buhari ya ce watannin da ke gaba na da matukar muhimmanci ga gwamnatinsa, musamman a fannoni guda uku da suka hadar da tsaro, tattalin arziki da kuma ci gaba da yaki da rashawa a duk fadin kasar.
A wani bangare na jawabinsa, Muhammadu Buhari ya ce ya zama wajibi ga ‘yan Najeriya su tabbatar da cewa ‘yan siyasa ba su yi amfani da su domin tayar da fitina a lokacin wadannan zabuka da take ba.
Shugaban ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da ya ce ya samu a cikin shekaru 7 da suka gabata, sannan ya ce yana murna ga wadanda ke yaba wa kokarin da ya yi da ma wadanda ke sukar salon mulkinsa.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 12 hours 21 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 41 minutes 46 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com