Kamfaninon tsaro a Nijeriya sun kama jirgin ruwa makare da danyen mai na sata a yankin Naija Delta

Kamfanonin tsaron Najeriya ta bai wa kwangilar tsaron bututan man fetur sun kama jiragen ruwa da mota maƙare da man da hukumomi suka ce na sata ne a yankin Neja-Delta da ke kudancin ƙasar.

Wata sanarwa da kamfanin mai na kasar, NNPC Limited, ya fitar a ranar Asabar ta tabbatar mutum huɗu aka kama yayin samamen.

Kamfanin ya samu rahoton sirri game da ayyukan mutanen tun a ranar 22 ga watan Disamba.

Dakarun tsaro sun isa wurin kuma suka tarar da su suna jigilar man ta ɓarauniyar hanya tare da tace gas a wata matata da ke Agge.

Tuni hukumomi suka ƙona jirgin da kayan da yake ɗauke da shi.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com