Home General Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa...

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa 61 dauke da makamai a jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa 61 dauke da makamai a jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami nasarar kama ‘yan daba 61 dauke da makamai da ake zargi da tada hargitsi, a kokarin rundunar dajike dukkan ayyukan Ta’addanci lokaxin yakin neman zabe.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Mamman Dauda, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna-Kiyawa, ya raba manema labarai a Kano.

Yace kame ya biyo baya umarnin babban sifeton
Janar na ‘yan sanda Nijeriya Usman Alkali-Baba, domin tabbatar da gudanar da ingantaccen zabe gami da dakile ayyukan daba a yayin zabe.
“wadanda ake zargin an kamasu ne a ranar 4 ga watan Janairu, yayin wani atasaye kakkabe barna a lokacin yakin neman zabe a filin wasa na Sani Abacha.

Yace an kwato makamai a hannun wadanda ake zargin da suka hadar da wukake 33, adduna 8, almakashi 4 sai kuma kunshin tabar wiwi guda 117.
Kwamishinan ya kara da cewa, kafin a fara gudanar da aikin, an gudanar da taron kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin zabe da kuma taron zaman lafiya da ya kunshi dukkan masu ruwa da tsaki.
“An kuma gudanar da tarurruka da masu ruwa da tsaki akan zabe a kananan hukumomi, da kuma ofishoshin ‘yan Sanda.
“Shugabannin jam’iyyar siyasa da ‘yan takarkaru sun yi alkawarin bawa ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a jihar domin samun ingantaccen zabe mai inganci,” in ji shi.
Dauda ya yabawa al’ummar jihar da sauran hukumomin tsaro da kafafen yada labarai da kungiyoyin ‘yan masu zaman kansu da masu ruwa da tsaki a harkar ‘yan sanda bisa addu’o’i da goyon baya da karfafa gwiwa da hadin kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp