Home General Kwankwaso yace zai ingata fannin Ilimi idan ya zama shugaban Nijeriya

Kwankwaso yace zai ingata fannin Ilimi idan ya zama shugaban Nijeriya

Abuja – Dan takarar shugaban kasa a inuwar New Nigerian Peoples Party, Rabiu Kwankwaso, yace idan ya ci zabe, gwamnatinsa zata gina Azuzuwan karatu 500,000 ga yara kanana marasa galihu.

Kwankwaso ya dauki wannan alkawarin ne ranar Litinin a wurin kadammar da kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, (PCC), a birnin tarayya Abuja.

Haka nan Kwankwaso ya bayyana cewa gwamnatinsa zata tabbata manyan makarantun gaba da Sakandire sun kai matakin gogayya a duniya.

Kwankwaso yace “Bari na tuna mana cewa a shirye muke mu sauya bangaren ilimi domin mu inganta shi kuma kowa ya samu damar neman ilimi. Musamman zamu gina Azuzuwa 500,000 a sassan jihohin kasar nan.”

“Zamu zuba kananan yara sama da miliyan 20m dake gararamba a sabbin Azuzuwa domin muna da kudirin kawar da su daga yawo a Titunan Najeriya. Zamu maida duk wani Fam na neman gurbi da ɗaukar aiki kyauta.”

“Jarabawar gama Sakandire da ta share fagen shiga manyan makarantu kamar WAEC, NECO, NABTEB, NBIAS, JAMB da sauransu zamu maida su kyauta ga ‘yan Najeriya.”

Da yake tabo Jami’a, kwalejin fasaha da sauran manyan makarantun gaba da sakandire, tsohon gwamnan jihar Kano ya ci gaba da cewa:

“Zamu inganta tare da fadada jami’oi, kwalejojin fasaha, da baki daya kwalejojin mu na ilimi kuma mu daga darajarsu su kai matakin gogayya a duniya. SH

NNPP ta kaddamar da shafin tallafawa kamfen Kwankwaso

Bayan haka, jam’iyyar NNPP mai kayan marmari ta kaddamar da bude shafin yanar gizo na hada kuɗi domin taimaka wa yakin neman zaben shugaban kasa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp