Home General Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara...

Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara a Gidan Man NNPCL Na Jihar Kano

Zargin sayar da man fetur ba bisa ka’ida bay a haddasa tashin wata gobara a gidan mai mallakin kamfanin NNPCL dake shatale-talen kano Club dake jihar kano a Arewa maso yammacin Nijeriya.
Wannan dai iftila’I na zuwa ne daidai lokacin da Al’umma jihar da wasu jihohihin dake kasar ke fama da matsalar karanci da tsadar manfetur sakamakon rashin tartibin farashin sa.
Shaidun gani da ido sun tabbatar wa da PRNigeria cewa bayan kammala zuba man ne a wata mota kirar Sienna wadda aka yi mata Karin tanki ne lamarin ya auku.
Sai dai duk da kokarin hukumar kashe gobara na dakile yaduwar gobarar lamarin sai da ya kai ga konewar motar kurmus.
Wani shaida ma da lamarin ya faru gaban idon sa wanda ya bukaci a sakaye sunan  sa sakamakon alaka da yake da ita da gidan man yace, ana tsaka da zuba man ne hukumomin gidan man suka hangi hukumar tsaro ta farin kaya dake yawo domin ganin an sayar da man yadda yake a farashin da gwamnati ta bayar, nan ne a kokarin su na gaggauta boyewa wutar ta tashi a motar.

Ba wannan ne karon farko da gobara ke tashi a gidajen man dake jihar kano ba sai dai a iya cewa wannan yazo da sauki domin kawo yanzu babu wani rahoton asarar rayuka sakamakon gobarar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp