An bankado manyan kabari dake dauke gawar mutane 49 a Kasar Congo MDD.

Majalisar dinkin duniya ta bayyana cewa an sami wani babban kabari dake dauke da mutane 49 a Arewa maso gabashin kasar Kwango.
Mataimakin kakakin majalisar Farhan Haq ne ya bayyana hakan ga manema labarai a birnin New na kasar Amurka, inda yace an sami kaburran ne a wasu kauyuka 2 a yankin Ituri dake da nisan kilo miter 30 da birnin Bunia.
An sami adadin mutane 42 da suka hadar da yara 6 a wani babban kabari a kauyen Nyamamba, haka kuma an ga wasu gawarwaki maza 7 a kauyen Mbogi, a cewar Haq.
Hukumomin yankin sun bayyana cewa kungiyar ‘yan bindiga ta CODECO sun kuma yi awon gaba da wasu mata a hare-haren da aka kai kauyukan.
Ko dai a watan Yulin daya gabata, kungiyar ta CODECO su 7 suka sanar da kawo karshen cin zarafin fararen hula a garin Ituri, musamman Djugu inda suke da karfi. Amma duk da haka suka cigaba da kai hare-hare a yankin.
Akalla mutane 195 ne aka hallaka tun watan disamba a jirin hare-haren da ake zargin kungiyar CODECO da wasu kungiyoyi mas dauke da makamai a cewar MDD. Haka kuma fiye da mutane miliyan 1.5 suka rasa matsugunnin su a lardin Ituri biyo bayan hare-haren.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 20 hours 58 minutes 47 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 40 minutes 12 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com