Home General Majalisar wakilai tace za’a kamu Mata Emefiele

Majalisar wakilai tace za’a kamu Mata Emefiele

Shugaban Majalisar Wakilan, Femi Gbajabiamila ya bayyana fushinsa kan yadda gwamnan babban bankin ya ki halartar zama tare da wani kwamitin wucen-gadi na majalisar karkashin jagorancin Alhassan Ado Doguwa.

A cikin wata wasika da Emefiele ya aike wa zauren majalisar a wannan Alhamis ya bayyana cewa, ba zai samu damar halartar zaman ba.

Majalisar Wakilan ta gayyace shi domin yi mata bayani game da gazawar bankin na CBN wajen wadata sassan Najeriya da sabbin takarddun kudin Naira a daidai lokacin da wa’adin ranar 31 ga watan nan na Janairiu na daina amfani da tsoffin kudin ya kusan cika.

.

Da dama daga cikin ‘yan Najeriya na farbagar halin da za su tsinci kansu a ciki muddin wa’adin daina amfani da tsoffin Naira ya kawo karshe ba tare da sauya musu da sabbin ba, lamarin da masana tattalin arziki ke cewa, zai jefa miliyoyin mutanen kasar cikin talauci.

Gwamnatin tarayya ta ce, ba za ta tsawaita wa’adin ba kamar yadda ‘yan kasar suka bukata, yayin da ‘yan kasuwa ke kokawa kan rashin musanya musu tsohuwar Nairar da sabuwa a bankunan kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp