Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci yan kasar da su ba shi kwanaki bakwai kacal domin magance matsalolin kuɗi da ake fuskanta a kasar.
Shugaban ya bayyana haka ne a wani taro da ya yi da ƙungiyar gwamnonin Jam’iyyar APC bayan wata ziyara da suka kai masa domin neman mafita kan ƙarancin kuɗin da ake fama da shi waɗanda suka ce hakan na barazana kan ayyukan alkhairi da gwamnatin ta yi.
Read Also:
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Malam Garba Shehu ya fitar, Shugaban ya ce sauya fasalin kuɗin da aka yi zai haɓaka tattalin arzikin ƙasar da kuma samar da tagomashi na tsawon lokaci ga ƙasar.
Haka kuma shugaban ya nuna damuwa kan lamuran wasu bankuna a ƙasar inda ya ce kansu kaɗai suka sani kuma a cewarsa ko shekara guda aka ƙara, matsalolin da suke tattare da san kai da zari ba za su gushe ba.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1465 days 11 hours 42 minutes 11 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1447 days 13 hours 23 minutes 36 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com