Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sakai 41 a Jihar Katsina

Mazauna wasu kauyuka da ke karamar hukumar Bakori a Jihar Katsina na zaman makoki sakamakon rasa yan uwansu da dama.

Hakan na zuwa ne yayin da wasu yan ta’adda suka kashe a kalla Yansakai 41 tare da raunata 2 yayin wani artabu a dajin Yargoje.

Rundunar yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da afkuwar lamarin tana mai cewa Yansakai din sun bi yan ta’addan daji ne da nufin kwato shanu da suka sace.

Jihar Katsina – Wani artabu da aka yi tsakanin yan ta’adda da kungiyar tsaro ta yan sa kai da aka haramta ayyukansu ya yi sanadin mutuwar a kalla mutum 41 a Katsina.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan Katsina, SP Gambo Isah ya tabbatar da aukuwar lamarin ta cikin wata  sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.

Yansakai sun bi sahun yan bindigan ne bayan sun sace shanu Ya ce yan haramtaciyyar kungiyar ta Yansakai daga kauyuka 11 a karamar hukumar Bakori, sun hadu sun bi sahun yan ta’addan da nufin karbo shanu da suka sace.

Mai magana da yawun yan sandan ya ce mambobin haramtaciyar kungiyar sun bi sahun yan ta’addan sun gano su a wani wuri a dajin Yargoje inda yan ta’addan suka musu harin kwaton bauna.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 26 minutes 51 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 8 minutes 16 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com