Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya ta kama masu Safarar mutane a jihar Kano

Rundunar sojin ruwa ta Najeriya ta kuɓutar da mutum 18 da aka yi safarsu a unguwar Rijiyar Lemu da ke ƙaramar hukumar Ungogo a jihar Kano da ke arewacin Najeriya

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktar yada labaran ta AO AYO-VAUGHAN Commodore ya fitar, wadda tace ta kama mutum biyu da take zargi da hannu wajen safarar mutanen.

Rundunar ta ce ta samu nasarar kuɓutar da mutanen ne bayan da wani jami’insu ya ankarar da su kasancewa ‘yar uwarsa na daga cikin mutanen da aka yi safar tasu.

Sojojin ruwan sun ce sun miƙa mutanen tare da waɗanda ake zargin hannun hukumar da ke yaƙi da safarar bil-adama ta ƙasar domin ɗaukar mataki.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 54 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 36 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com