Gwamnatin Nijeriya ta bada Umarnin Rufe Jami’oin Kasar Saboda Zaben 2023

Wata sanarwa da Hukumar Kula da Jami’o’i ta Najeriya ta fitar ta umurci a rufe dukkanin jami’o’in ƙasar tsawon lokacin da za a gudanar da babban zaɓen ƙasar na 2023.

Sanarwar, wadda ta samu sa hannun mataimakin shugaban hukumar, mai kula da harkar gudanarwa, Chris J. Maiyaki, ta ce za a rufe jami’o’in ne domin kare lafiyar ma’aikata, da ɗalibai a tsawon lokacin zaɓen.

Bayanin ya ce umurnin ya fito ne daga ministan ilimi na Najeriyar, Adamu Adamu, inda aka umurci dukkanin shugabannin jami’o’i su rufe daga 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris.

Matasa dai na daga cikin mafiya yawa a kundin rajistar zaɓen Najeriya, kuma ana sa ran za su taka muhimmiyar rawa a babban zaɓen mai zuwa.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 14 hours 28 minutes 3 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 9 minutes 28 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com