Home General Gwamnatin jihar Katsina ta kafa kwamitin Binciken musabbabin kisan ‘yan Banga a...

Gwamnatin jihar Katsina ta kafa kwamitin Binciken musabbabin kisan ‘yan Banga a jihar

Gwamnan jihar Katsina da ke arewa maso yamacin Najeriya Aminu Bello Masari ya kafa kwamiti mai mambobi 13 da zai gudanar da bincike kan kisan ‘yan sa kai sama da 100 da aka yi a wasu garuruwan ƙananan hukumomin Kankara da Bakori a jihar.

A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran gwamnan Al-amin Isa, ya aike wa manema labarai, ya ce ana sa ran kwamitin ƙarkashin jagorancin Hon. Justice A.B. Abdullahi, zai gudanar da bincike domin gano abun da ya haddasa kashe-kashen a waɗannan garuruwa.

Sauran ayyukan da ake sa ran kamitin zai gudanar sun haɗa da yin bincike domin gano adadin rayuka da dukiyoyin da ka rasa a lokacin kashe-kashen.

Tare da gano yawan mutanen da harin ya shafa sannan da gano ƙungiyoyi ko mutanen da ke da suka aikata ko suke da hannu wajen wannan aika-aika.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnati na duba yiyuwar tallafa wa waɗanda lamarin ya rusta da su tare da iyalan mamatan, da bayar da shawarar ɗaukar matakan kare kai da bai saɓa wa doka ba, tare da ɗaukar matakai domin kare aukuwar makamancin wannan hari a nan gaba a jihar.

A makon da ya gabata ne dai rahotonni suka ce ‘yan bindiga sun yi wa wasu ‘yan sakai waɗanda ke ƙoƙarin ƙwato wasu shanun sata, kwanton ɓauna tare da kashe sama da 100 a wasu garuruwa a ƙananan hukumomin Kankara da Bakori a jihar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp