Kotun Koli ta Gargadi ‘yan Nijeriya

Kotun Ƙolin Najeriya ta gargaɗi masu sukarta game da hukuncin da ta yanke da ya bai wa shugaban majalisar dattawan ƙasar Sanata Ahmada Lawan da Sanata Godswill Akpabio, nasara a matsayin halastattun ‘yan takarar sanata a jam’iyyar APC.

Kotun Ƙolin dai ta umarci hukumar zaɓen ƙasar INEC da ta amince da sunayen sanatocin biyu a matsayin ‘yan takarar kujerun sanata a jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar a babban zaɓen ƙasar da ke tafe ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki.

Tun bayan wannan hukunci ne dai mutane ke cigaba da sukar kotun da ɓangaren shari’ar ƙasar, ciki har da fitaccen marubucin nan Farfesa Faroq Kperogi, ɗan Najeriya mazaunin Amurka.

A wata sanarwa da Kotun Ƙolin ƙasar ta fitar da hannun daraktan yaɗa labaranta Dakta Festus Akande ta gargaɗi masu sukar kotun da su guji aikata hakan.

Kotun ta jadadda cewa ”Mu ba ‘yan siyasa ba ne, kuma ba za mu zama ‘yan siyasa ba, dan haka bai kamata a ɗauke mu a wannan matsayi ba. Babu ra’ayin wani mutum da zai fi ra’ayin kowa. Najeriya gaba take da kowa- da-kowa, dan haka waɗannan kalamai sun isa haka”.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 15 hours 4 minutes 10 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 45 minutes 35 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com