Home General Buhari ya bukaci a bar ‘yan Nijeriya suke zuwa Dubai

Buhari ya bukaci a bar ‘yan Nijeriya suke zuwa Dubai

Shugaba Muhammadu Buhari ya sa baki a dambarwar diflomasiyya da ke tsakanin Najeriya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), wadda ta kai ga ƙasar ta Gabas ta Tsakiya ta dakatar da bai wa ‘yan Najeriya takardar izinin shiga cikinta, wato biza.

A wata tattaunawa ta waya da Shugaba Buhari ya yi ranar Litinin da takwaransa na Daular, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, wanda kuma shi ne Sarkin Abu Dhabi ya yi maganar neman ɗage dakatarwar.

Tattaunawar da Shugaba Buharin ya yi da Sheikh Al Nathan na ƙunshe ne a wata sanarwa da kakakin shugaban na Najeriya Mallam Garba Shehu, ya fitar yau Talata

A watan Oktoba na shekarar da ta wuce ne 2022 hukumomin Daular suka dauki matakin dakatar da bai wa ‘yan Najeriya bizar, sai wadanda suke da fasfo na manya wato na diflomasiyya kawai.

Duk da cewa hukumomin ƙasar ta Larabawa ba su bayyana dalilinsu na ɗaukar matakin ba, wasu na danganta shi ga rashin ɗa’a da bin doka da oda da wasu ‘yan Najeriyar da ke zaune ko aiki a can suke yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp