Home General CBN yace suna nan akan bakar su na daina karbar Tsoffin Kudi

CBN yace suna nan akan bakar su na daina karbar Tsoffin Kudi

Gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya ce har yanzu suna kan bakarsu na wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu game da daina karbar tsoffin takardun kudi a fadin kasar.

Emefiele na bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi ga jami’an diflomasiyya na kasashen duniya a ma’aikatar harkokin wajen Najeriya da ke Abuja, babban birnin kasar.

“An fara samun sassaucin karancin kudin da ake fama da shi a sassan kasar, sakamakon karba da ake yi a banki wanda hakan ke nufin sabbin takardun kudi sun wadata, saboda haka babu dalilin kara wa’adin ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi,” in ji Emefiele.

Wannan matakin dai ya kara jefa al’ummar Najeriya cikin rudani, bayan da kotun kolin kasar ta wa’adin zuwa ranar 15 ga watan Fabrairu, kafin ta yanke hukunci na karshe. Sai dai Gwamnan Babban Bankin na wannan jawabi daidai lokacin da wasu bankuna a kasar suka daina karbar tsofaffin kudin a hannun Al’umma wanda hakan ke alamta cewa Al’umma kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp