Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun kudi.

Karamin Ministan Kwadago da aiki Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC da suka yi adawa da gwamnatin Muhammadu Buhari a kotun koli. Festus Keyamo, babban lauyan Najeriya, ya ce ta hanyar ayyukansu, gwamnonin APC suna “yaki ne da sunan talakawa, suna fafutukar ganin jama’a su samu taimako” a kan manufofin gwamnatin.

“Duk gwamnan da ya je kotu yana gwagwarmayar talakawa, yana fafutukar ganin jama’a su samu tallafi, dukkansu gwamnonin APC ne,”kalaman Minista  Keyamo.

A makon da ya gabata ne gwamnoni uku karkashin jam’iyyar APC, Kaduna, Kogi da Zamfara suka maka gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC a kotun koli, inda suka bukaci a sauya wa’adin da aka sanya na amfani da tsofaffin takardun kudi na naira. Babban bankin Najeriya ya sanya ranar 10 ga watan Fabrairu a matsayin wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1,000.

A bisa karar da gwamnonin APC suka shigar, kotun koli ta bayar da umarnin dakatar da wa’adin, umarnin da gwamnatin tarayya ta yi watsi da shi.

Sai dai kuma wasu Jihohi biyu da PDP ke jagoranta su ma sun bi sahun gwamnatin tarayya.

Minista Keyamo, wanda kuma shi ne mai magana da yawun jam’iyyar APC na yakin neman zaben shugaban kasa, ya ce karar da gwamnatocin jihohin APC suka yi alama ce ta tarayya ta gaskiya.

Ya ce gwamnonin APC su tashi tsaye wajen adawa da gwamnatin tarayya kan wannan manufa, hakan ya nuna cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu, idan aka zabe shi a ranar 25 ga watan Fabrairu a matsayin shugaban kasa, zai tabbatar da tsarin tarayya na gaskiya a kasar nan.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 50 minutes 21 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 31 minutes 46 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com