Home General Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun...

Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun kudi.

Karamin Ministan Kwadago da aiki Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC da suka yi adawa da gwamnatin Muhammadu Buhari a kotun koli. Festus Keyamo, babban lauyan Najeriya, ya ce ta hanyar ayyukansu, gwamnonin APC suna “yaki ne da sunan talakawa, suna fafutukar ganin jama’a su samu taimako” a kan manufofin gwamnatin.

“Duk gwamnan da ya je kotu yana gwagwarmayar talakawa, yana fafutukar ganin jama’a su samu tallafi, dukkansu gwamnonin APC ne,”kalaman Minista  Keyamo.

A makon da ya gabata ne gwamnoni uku karkashin jam’iyyar APC, Kaduna, Kogi da Zamfara suka maka gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC a kotun koli, inda suka bukaci a sauya wa’adin da aka sanya na amfani da tsofaffin takardun kudi na naira. Babban bankin Najeriya ya sanya ranar 10 ga watan Fabrairu a matsayin wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1,000.

A bisa karar da gwamnonin APC suka shigar, kotun koli ta bayar da umarnin dakatar da wa’adin, umarnin da gwamnatin tarayya ta yi watsi da shi.

Sai dai kuma wasu Jihohi biyu da PDP ke jagoranta su ma sun bi sahun gwamnatin tarayya.

Minista Keyamo, wanda kuma shi ne mai magana da yawun jam’iyyar APC na yakin neman zaben shugaban kasa, ya ce karar da gwamnatocin jihohin APC suka yi alama ce ta tarayya ta gaskiya.

Ya ce gwamnonin APC su tashi tsaye wajen adawa da gwamnatin tarayya kan wannan manufa, hakan ya nuna cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu, idan aka zabe shi a ranar 25 ga watan Fabrairu a matsayin shugaban kasa, zai tabbatar da tsarin tarayya na gaskiya a kasar nan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp