Home General An tabbatar da Mutuwar Sojojin Burkina Faso 50 sakamakon wani harin

An tabbatar da Mutuwar Sojojin Burkina Faso 50 sakamakon wani harin

Akalla sojojin Burkina Faso 51 ne aka tabbatar da cewa sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka samu raunuka, sakamakon wani harin kwanton bauna da ‘yan ta’adda suka kai wa dakaru a yankin Sahel kamar dai yadda rundunar sojin kasar ta sanar a wannan litinin.

Wannan lamari dai ya faru ne a ranar juma’a da ta gabata, inda da farko aka ruwaito cewa sojoji 8 ne suka rasa rayukansu, kafin wata sanarwa da rundunar sojin kasar ta fitar a wannan litinin ta bayyana gano karin gawarwakin wasu 43 a inda lamarin ya faru.

Sanarwar ta ci gaba da cewa an kashe ‘yan ta’adda akalla 167, bayan da rundunar sojin saman kasar ta kai daukin gaggawa domin taimaka wa dakarunta.

Hakazalika sanarwar ta ce an lalata ko kuma kwace makamai da kuma babura masu tarin yawa wadanda ‘yan ta’addan ke amfani da su a gumurzun da aka yi tsakanin garuruwan Deou da Oursi da ke yakin na Sahel.

Burkina Faso dai ta jima tana fama da hare-haren masus ikirarin jihadi musamman a yankin Arewaci da kuma gabashin kasar, yayin da wannan barazana ke ci gaba da yaduwa hatta a wasu yankuna da ke kudancin kasar iyaka da Jamhuriyar Benin, Togo da kuma Ghana.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp