Home General Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya

Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya

Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya baki daya, ga da bukatar yan kasar su gudanar da zabe cikin lumana.

Wannan na Wani sako na musamman da manyan jami’an gwamnatin kasar suka nada ta bidiyo mai tsawon mintina 58 suka kuma aikewa jama’ar kasar,

Sakon da ya janyo hankalin ‘yan siyasa da kuma jama’a baki daya da su bada gudumawa wajen ganin anyi zabe mai inganci a karshen wannan mako.

Cikin wadanda suka gabatar da sakonninsu a bidiyon sun hada da Sakataren harkokin waje Anthony Blinken da Babbar jami’ar USAID Samantha Power da Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Linda Thomas-Greenfield.

Sakon ya bayyana cewar ‘yan Najeriya sun sake samun wata dama na bayyana ra’ayoyinsu da kuma zabin shugaban da suke bukata ta hanyar zabe saboda muhimmancin kuri’un su.

Blinken yace muhimmancin wannan zaben da zai gudana a karshen wannan mako ba wai ya tsaya kawai ga Najeriya bane, har ma da duniya baki daya.

Wakilan gwamnatin sun jaddada cewar Amurka bata goyan bayan wani ‘dan takara guda, amma kuma tana goyan bayan shirin wanda zai baiwa jama’ar kasar zabin abinda suke so ta hanyar lumana.

Sakon yace samun gudanar da karbabben zaben cikin kwanciyar hankali zai taimaka wajen samun dorewar zaman lafiya a duniya baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp