Home General Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Majalisar tsaron Najeriya da shugaban Buhari ya jagoranta ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun dokoki na tarayya a ranar 25 ga watan Fabrairu, kamar yadda aka tsara.

Babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a na ƙasar Abubakar Malamin ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron majalisar a fadar shugaban ƙasar.

Malami ya ce babban hafsan tsaro na ƙasar Janar Lucky Irabor, da hafsoshin rundunonin sojin ƙasar uku tare da babban sifeton ‘yan sandan ƙasar sun yi wa majalisar bayani game da shirin da suka yi kan babban zaɓen da ke tafe ranar Asabar mai zuwa.

Ya ƙara da cewa ”dangane da haka, majalisar ta haɗu a kan cewa zaɓen na ranar Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara”.

Taron ya zo ne bayan, da taron majalisar magabata ta tabbatar da shirin hukumar zaɓen ƙasar da na ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a kan zaɓen na ranar Asabar mai zuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp