Home General An kai hare-hare 60 a lokacin yakin neman zaɓe – CDD

An kai hare-hare 60 a lokacin yakin neman zaɓe – CDD

Akalla hare-hare 60 aka kai tare kuma da kashe mutum tara a lokacin yakin neman zaɓe a faɗin Najeriya gabanin zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a gudanar a ranar Asabar.

Cibiyar Tabbatar da Dimokuraɗiyya da Ci Gaba CDD, ce ta bayyana hakan a cikin wani rahoto da ta fitar gabanin shiga rumfunan zabe domin kaɗa kuri’a, inda ta ce wasu da dama kuma sun jikkata a hare-haren da aka kai tun fara yakin neman zaɓe a watan Satumban 2022.

CDD ta ce batun rashin tsaro da ƙarancin man fetur da na kuɗi da kuma sauran abubuwa za su iya kawo cikas ga yadda zaɓen zai gudana.

“A karshen shekarar 2022, rikice-rikicen da ke da alaƙa da siyasa sun ƙaru tun bayan zaɓen 2019 da aa gudanar. Alkaluman da muka tattara ya nuna cewa an kai hari sau 60 a lokacin yakin neman zaɓe, inda mutum tara suka mutu,” in ji CDD.

Kungiyar ta kuma nuna damuwa kan yadda ta ce ‘yan siyasa na ɗaukar ‘yan bangar siyasa domin kawo cikas a zaɓen da za a gudanar, inda ta ce hakan zai ƙara janyo taɓarɓarewar matsalar tsaro.

Cibiyar ta yi kira jam’iyyun siyasa da su tabbatar da cewa mambobin da kuma magoya bayansu sun bi sahun sharuɗan da aka kwamitin zaman lafiya ya zartas yayin lokacin saka hannu a yarjejeniyar yin zaɓe lami lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp