Home General Muna sane da matsalolin da ake samu a rumfunan zabe-INEC

Muna sane da matsalolin da ake samu a rumfunan zabe-INEC

Shugaban hukumar zaɓen Najeriya (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya ce hukumar na lura tare da sanya ido game da yadda zaɓe ke gudana a faɗin ƙasar.

Ya ce hukumar ta samu rahotonnin wasu ‘yan matsaloli nan da can, to sai dai hukumar a shirye take wajen magance matsalolin.

A yau ne dai hukumar ke gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya.

Farfesa Mahmud ya ƙara da cewa burin hukumar shi ne tabbatar da samun sahihi da ingantaccen zaben a ƙasar.

Farfesa Yakubu ya ce wannan shi ne karo na farko da hukumar ke gudanar da zaɓen kamar yadda aka tsara ba tare da ɗage zaɓen ba.

Ya ce ana ci gaba da zaɓe a faɗin ƙasar, kuma na’urar BVAS da ake amfani da ita tana aiki yadda ya kamata a wurare da dama a faɗin kasar.

Ya ce rahotonnin da hukumar ke samu daga ofisoshin hukumar na jihohi da birnin tarayya na nuna cewa ƙorafe-ƙorafen da jama’a ke yi game da aikin na’urar BVAS na ci gaba da raguwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp